Wednesday, September 27, 2017

Tofa gawata sabuwa mutanan Nigeria

Don Allah A Ba Ni Amsar Wadannan Tambayoyin

Daga Hajiya Jamila Moh'd Mataimaki

Wai a ma'aikatun, CBN, NNPC, Kwastan, EFCC da sauran manyan ma'aikatun gwamnati ba a daukar sabbin ma'aikata ne da ba za a sanarwa da 'ya'yan talakawa su jaraba sa'a ba?

Me ya sa sai a bangaren aiyukan wahala ko na saida rai ko wanda babu wani albashi mai tsoka a cikin sa, kamar su soja, dan sanda, malamin makaranta da sauransu sannan za a sanar da 'ya'yan talakawa su je su nema?
Share:

No comments:

Post a Comment