Tuesday, October 3, 2017

AUREN FANSA CHAPTER 9 & 10

AUREN FANSA CHAPTER 9 & 10

Haka kuwa akayi washe gari da safe Hamza da
Bilki suka fita don saka Meenah a makaranta.
Gobarau Academy itace makarantar da suka nufa,
da zuwansu da komai basu wuce minti talatin ba
aka kammala komai aka saka ta Pre nursery, duba
da shekarunta kuma a k'a'idar makarantar idan
yaro bai kai shekara 3 ba to baza'a saka shi
nursery ba daman. Daman 'yan pre nursery ba'a
saka musu uniform.
A ranar aka barta makaranta kuma ko kuka batayi
ba da su Hamza zasu tafi don ta samu abin wasa
sai dad'i takeji.
K'arfe 12 suke tashi don haka dole Bilki ke d'auko
ta don Hamza na wurin aiki lokacin, ba yadda ta
iya haka nan take hak'ura tana d'auko ta d'in.
Haka rayuwar ta cigaba da gudana cikin hukunci
da hikimar ubangiji, Meenah har ta shiga nursery.
Meenah Allah ya bata k'walwa komai aka koya
mata ta iya sai dai idan ba'a koya mata ba, kuma
idan ta dawo gida ta dinga yi kenan ko gajiya
batayi.
Ba'a saka Zarah makaranta ba sai da Meenah ta
shiga nursery 2 a lokacin ita kuma Zarah tana da
shekara 3 a duniya yayinda Meenah keda hud'u.
Ranar wata juma'a akayi ma su Meenah hutu
suna zuwa gida Meenah ta fara neman babanta
don nuna mai report card nata, sai
dai rashin sa'a yayi tafiya zuwa Lagos a safiyar
ranar, tayi ta kuka tana kiran ita Baba.
Bilki tana tsaki ta ansa report card nata dana
Zarah tana dubawa, abin takaici a wurinta wai
Meenah na d'aya tayi ita kuwa Zarah na ashirin
tayi cikin su ashirin da shidda. Bilki kamar tayi
kuka don takaici. Wato Meenah dai tafi d'iyarta
k'ok'ari kenan?
"Gaskiya da sake!" Ta kalli Meenah tace mata "Ke!
Zo nan!" Meenah tayi tsaye idanunta k'wal hawaye
a duniya tana tsoron Bilki, fizgo ta tayi da k'arfi.
"Ke dan ubanki sai da kika yi na d'aya wannan
karon ma? Kin manta bugun da nayi maki last
term kenan? Salon kija babanta ya dawo ya zane
Zarah ko? Ke ga mai k'ok'ari ko? Shegiya mai
kama da mage! Wuce ki bani wuri!" Da gudu
Meenah tayi d'aki tana kuka sosai, jawo Zarah tayi
ta rungume tace.
"Don Allah d'iyar Baba ki dage kifi waccan
yarinyar k'ok'ari kinji?" Zarah ta gyad'a kai.
Da rana ta zuba ma Zarah abinci ta shiga wanka,
Meenah na zuwa Zarah tace.
"Zo muci." Ba musu ta zauna suka fara cin
abincin tare.
Ba'a jima ba Bilki ta fito wanka tana lek'owa taga
Meenah nacin abin da d'iyarta abinda ta tsana! Da
tsawa tace
"Ke!" A firgice Meenah ta tashi tana kyarma,
Bilki ta k'ara daka mata tsawa.
"Bana hana ki cin abinci tare da Zarah ba?
Shegiya wuce ki tafi d'aki." Tayi d'aki da gudu a
tsorace. Zarah ta aje cokalin hannunta tace
"Bazan ci ba nima sai da Meenah." Daman Bilki
tasan abinda zatace kenan, tsaki taja tace
"To sai dai kar kici wallahi amma bazakici tare da
Meenah ba, kinji na fad'a miki!"
Aikuwa aje cokalin tayi tana fushi sosai ta bar
parlon. Tsaki Bilki ta k'ara yi tana k'ara jin
haushin Meenah...
***
Sauri yakeyi ya dawo gida don nuna ma iyayensa
result nasa na shedar kammala jss3 nasa. Driver
na yin parking ya fito da gudu yana murna
shigarsa keda wuya ya taradda abinda ya d'aga
masa hankali, ya kuma gigita shi a lokaci guda,
take zuciyarsa ta fara bugawa da sauri a yayinda
k'walwarsa ta tsaya cak! ta bar aiki lokaci d'aya!!!
Iyayensa ne kwance jina jina, a yayinda wasu
mutane kusan su bakwai ke tsaye cikin bak'ak'en
kaya hartta fuskokinsu an rufe da black mask!
Tsaye yayi ya kasa tantance a wace duniyar yake,
take kuma ya fashe da kuka yana fad'in.
"Su waye ku? Mey...asa ku...ka kashe min
iyaye?"
Direwa yayi k'asa yana kuka yana jijjiga iyayen
nasa a yayinda yake kiran Anisah! Mutumin yayi
dariya yace.
"Ka bar kuka yaro, sun tafi inda ba'a dawowa
kaima kuma yanzu zaka bisu!" Yakece da dariya
sannan ya saita bindigar daodai saitin k'irjinsa ya
harba.
A gigice ya farka duk da Ac d'in da ke aiki amma
hakan bai hana sa yin sharkaf da zufa ba. Ta6a
jikinsa ya soma yi amma baiga jini ba, ajiyar
zuciya ya sauke ya shiga yin addu'a don ba
k'aramin tsoro yaji ba.
"Wane wane irin mafarki ne haka..... ?"
Ya fad'a yana mai k'ara tunawa da mafarkin da
yayi. Zumbur! Kuma ya mik'e ya fice da gudu don
duba lafiyar iyayensa don gani yake kamar da
gaske ne....!
"Mummy...! Mu.." A firgice suka farka daga bacci,
da mamaki suka ce
"Waye?" Kasancewar d'akin gauraye yake da duhu
fitila a kashe take, Daddy ya kai hannunsa ya
kunna bedside lamp yana kallon Faruk dake tsaye,
da sauri Faruk ya rungume mahaifiyar tasa yace.
"Alhamdulillah! Ashe duk lafiyarku lau, wallahi naji
tsoro."
Mummy tayi murmushi don tasan ya k'ara yin
mafarki. Tace
"Faruk nasha fad'a maka mafarki ba gaskiya bane
ka daina d'aga hankalinka akan mafarki, nasha
fad'a maka bakaji."
Faruk yace
"Nasani Mummy amma meyasa a duk lokacin da
nayi mummunan mafarki sai naji gabana ya fad'i,
sannan na kasa samun nutsuwa, gani nake kamar
wani abu na shirin faruwa da mu!"
Daddy yace
"Haba Faruk! Ka zamo mai tawwakali mana, an
fad'a maka mafarki ba gaskiya bane haba! Tashi
kaje ka kwanta."
Sum sum ya tashi ya fice, Daddy ya kalli Reemah
yace.
"Wai shin kuwa yaron nan na addu'a a duk
lokacin da zai kwanta bacci?"
Reemah tace
"Yana yi, kullum sai na je na tabbatar da sai
sunyi addu'a kafin su kwanta su duka."
Daddy ya numfasa yace
"To Allah ya kyauta amma sai ya k'ara dagewa da
addu'a sosai."
Reemah tace
"Insha Allah."
***
BAYAN WATA D'AYA
Zaune yake yana karatu wayarsa ta fara k'ara,
ganin sunan Daddynsa yasa yayi saurin d'agawa.
"Hello kaine Faruk?"
Yace
"Eh nine lafiya ina mai wayar nan?"
"Sai dai kayi hak'uri mai wayar nan ya rasu dashi
da matarsa!"
"What? Innalillahi wa'inna ilahir raj'un!"
"Ya Faruk!"
A firgice ya farka ganin Anisha tsaye gabansa tana
kakkarwa, yasa yace
"Ke lafiya menene?"
Ta fashe da kuka.
"Mummy! Ya Faruk Daddy da Mummy babu."
Yace
"Kamar ya? Ina suke?"
Tace
"Wasu mutane na nan sun zagaye Mummy da
Daddy..."
Kafin ta k'arasa ya mik'e da gudu ya fita."
Zuwansa keda wuya ya taradda abinda ya d'aga
masa hankali lokaci guda kuma ya gigice ya shiga
rud'ani! Murza idanunsa ya fara yi don yayi
tunanin wannna karon ma mafarki yakeyi, la6ewa
ya shiga yi a bakin k'ofa yana sauraren mutanen
da ke tsaye. Kusan su hud'u majiya k'arfi.
"Hello Hajiya Laila Sunusi! Aikin da kika samu fa
an kammala abu biyu ya rage. Na farko bamuga
yaransu guda biyu da kika lissafa mana ba! Na
biyu takardun gidannan da sauran mahimman
takardun da kika ce a baki."
"Yes Ma! Ok Ma! Insha Allah na miki alk'awarin
cika miki dukkan aikin da kika
samu da ke da aminiyarki ya sunan ta ma? Haha
yes Bilkisu Ringim! Ok..."
Kamo hannun Anisah yayi yana kuka d'akinsa ya
fad'a ya kwashi wasu takardu nasa dashi dana
Anisah na makarantarsa da abubuwan da yake
buk'ata ya jefa jikka suka fito da sauri sukayi
hanyar fita. Anisah na kuka shima yana kuka suka
fito gate, gaba d'aya masu gadinsu basu nan,
security sunfi goma amma yanzu bai ga kowa ba.
Adaidaita ya samu suka wuce wata police station,
yana zuwa ya fad'a masa dukkan abinda ya gani
ya kuma ji sannan yace suzo su ceci iyayensa
kafin su mutu.
Ba 6ata lokaci suka nufo gidan sai dai da
zuwansu abin mamaki ba komai gidan asali ma
gidan a rufe yake da kwad'o sai dai gawar
iyayensa, nan akayi examining d'insu aka tabbatar
da basuda rai, take Faruk ya rasa a wace duniyar
yake, kansa yayi dip, hawaye kuwa kamar an
bud'e pampo. Sambatu kawai yakeyi yana fad'in.
"Daman nasha yin mafarki an kashe mana iyaye!
Nace abin kamar zai faru amma ba wanda ya kula
ni..."
Duk police d'in da yayi yunk'urin tab'asa da
niyyar rarrashi turesu yakeyi suna fad'uwa k'asa,
gaba d'aya kamar ya zauce. Yama k'i nutsuwa
asan ina danginsa suke a sanar masu de abinda
ya faru. Gaba d'aya gidan ba mota ko d'aya,
motocin mahaifinsa sunfi kala takwas amma
yanzu ko d'aya babu.
Nan kuma kan Faruk ya fara juyawa kafin ya
ankara ya fad'i k'asa tim!
Share:

No comments:

Post a Comment