Saturday, September 30, 2017

AUREN FANSA CHAPTER 5 & 6

AUREN FANSA CHAPTER 5 & 6
BAYAN KWANA BIYU
Ranar suna yarinya taci sunan mamanta
marigayiya Amina, daman bawani taron sunan da
akayi wane taro ma ana zaman makoki?
Amina duk da tana jaririya Allah ya zuba mata
hak'uri ga bata kuka sosai sai dai idan taji yunwa
ko wani abin na damunta. Kammaninta sak na
mahaifiyarta ta d'ebo hartta gashinta irin nata ne
lub lub, hasken ne kawai bata d'ebo ba sa6anin
marigayiya da take fara tas kamar yayanta Hamza
amma Amina babyn ita ba fara bace tas, sai dai
tana da kyau duk da batada hasken ana ganin
kyawunta. Idan ta bud'e ido ta kalli mutum zaka
gansu manya ne farare tas!
Baya 'yan kwanaki a lokacin Amina ta kwana 20
cif a duniya Goggo ta kira Hamza da Bilki gidanta
akan cewa tana son magana dasu.
Bayan sun iso suka gaisa Goggo ta d'auko Amina
dake kwance kan gado tana bacci, ta mik'a ma
Hamza ita tana murmushi tace
"Hamza kamar yadda kasani marigayiya ta baka
amanar rik'on Amina kuma ka d'auki alk'awarin
haka, don haka yau na damk'a maka Amina a
matsayin d'iyarka halak malak, da fatan zaka rik'e
ta bisa amana."
Sai kuma ta juyo ta kalli Bilki tace
"Bilkisu ga amanar Amina nan ki rik'e ta amana
saboda kar ki manta marainiya ce gaba da baya
idan har kika ci zalinta Allah zai mata sakayya."
Hamza yace
"Insha Allah Goggo kar ki damu ina k'auanar
Amina kamar 'yar dana haifa haka nake jinta a
raina. Insha Allah zamu rik'e ta amana, Allah ya
taya mu rik'o."
Goggo tace
"Amin, daga cikin dukiyar da mahaifinta ya bar
mata a ciki ake siya mata su pampers da su
madara, sai kayan sawa da sauran abinda ba'a
rasa ba, amma ba kasafai nake amfanin da kud'in
ba sai idan ba kud'i hannuna, amma tunda yanzu
zata dawo hannunku da zama sheyasa zan
damk'a maka kud'inta a hannunka ka adana mata
ko ka juya mata su duk yadda kaga ya dace."
Jiki a sanyaye Hamza yace
"Insha Allah Goggo."
Daga haka Goggo ta tashi ta had'o kayan Amina
tas sannan ta kira mai gadinta ya saka cikin mota.
Sai da suka ci abincin rana sannan suka koma
gida, inda ko a mota Bilki ce ta rik'e Amina
sannan ga mamakin Hamza bata nuna komai ba
har rungume ta tayi tana fad'a ma Hamza d'iyar ta
shiga ranta sosai. Ba k'aramin sanyaya mishi
zuciya hakan yayi ba, duk wata fargaba dake ransa
ta kau yadda yaga Bilki na tarairayar Amina kamar
'yar cikinta.
Bayan sun koma gida da daddare Bilki ta had'a
ruwan zafi tayi ma Amina wanka tas sannan ta
shirya ta cikin kayan baccinta wato overall pink
wadda tayi mata kyau, gashin babyn ya wani yi
irin pam d'innan sannan duk da haka a nannad'e
yake gwanin kyau.
Bayan ta gama ta had'a mata madararta ta bata
tasha ta k'oshi, sannan ta rirrigata ta tayi bacci,
duk akan idon Hamza wanda yake mata kallon
mamaki, abinda baiyi zato ba yau gashi Bilki
nayi.
Bayan ta rirriga Amina tayi bacci zuwa tayi kusa
da Hamza tana rok'on gafarar abubuwan da ta
masa, bai gasgata ba sai da ya ga Bilki na kuka
sosai tana rok'onsa, take ya yarda ta yi nadama
don haka sai ya yafe mata suka shirya.
Haka cikin dare da Amina tayi kuka Bilki zata
tashi ta bata madara har ta koma bacci, gashi
sam bata kukan dare yunwa kad'ai ke tashinta da
kuma an bata madara zata koma shikenan kuma
sai asuba.
Da safe ma haka tayi mata wanka tas ta bata
madararta, koda wasa Hamza bai yi tunanin za'a
samu wata matsala ba daga wurin Bilkin ba.
Don haka sai ya saki jikinsa ya manta da maganar
k'arin aure.
Duk sadda Hamza ke gida to Amina na hannunsa
yana mata wasa, yana ce mata
"Meenah!" Ya bata madara, ya chanza mata
pampers, ya mata tsarki, sannan ya rirriga ta har
sai tayi bacci.
A haka har sunan ya bita don Hamza Meenah
yake ce mata idan yana mata wasa.
Watan Meenah biyar amma ta zama wata irin
k'atuwa tayi nauyi sosai, da k'yar ake d'aga ta, ga
bata wasa da abinci komai ci takeyi, sai dad'a
kyau takeyi kullum.
Hamza na matuk'ar nuna mata kulawa kullum
yana manne da ita especially weekends ranar da
ba aiki, baya zuwa ko ina zai zauna gida yana
kula da Meenah. Sannan komai yana siya mata
daidai gwargwado bai ta6a nuna gazawarsa ba,
tsaye yake kai da fata wajen ganin Meenah ta taso
cikin ingatacciyar rayuwa.
Watan Meenah bakwai daidai Bilki ta samu ciki,
Allah cikin ikonshi cikin baya bata wahala, murna
had'e da godiya ga Allah suka yi ba adadi.
Zo kuga zakwad'i da rawar kai wurin Bilki. Tun
cikin bai tasa ba ta fara siyayyar kaya kamar
hauka a 6oye, tasan Hamza zai bata kud'i idan
lokacin yayi amma tsabar son abin duniya yasa
bata iya hak'uri. Ko kuma ta d'auka idan ya aje da
yake bai ta6a tunanin tana masa sata ba sheyasa
bai farga ba, sai dai idan yaga kamar kud'in ba
daidai suke ba yayi ta tunanin yadda akayi ya
kashe su.
***
Faruk ne kwance bisa gadonsa na alfarma yayi ruf
da ciki yana game cikin system d'insa. Sai yanzu
na k'are ma d'akin nasa kallo, color d'in d'akin
dark da light blue ne, hartta gadonsa blue ne da
bed-sheet d'in da ke shimfid'e a sama. Carpet
d'in da ke shimfid'e a d'akin blue ne. Gefe guda
kuma study table ne shima blue, sai cikin wata
k'atuwar box kayan wasansa ne wanda mafi yawa
nafi hango jirgin wasa kala kala, hartta kan
gadonsa jirgin wasa ne yakai biyar gefensa, d'aya
kuma a hannunsa, a raina nace to shi kuma son
jirgi yake?
Mummy ce tsaye bakin k'ofa tana kallonsa kafin
kuma ta k'araso tare da zama a kusa dashi ta
dafa shi.
Juyowa yayi yana kallonta kafin yace.
"Mummy na."
Murmushi tayi tana shafa gashin kansa sannan
tace
"Faruk ya naga kana game? Ba nace kazo ka koyi
hardarka ba, ba gobe zaka bayar ba a islamiyya?"
Murmushi yayi yace
"Nayi Mummy."
Tace
"Anya Faruk?"
Yace
"Allah yanzu na gama."
Tace
"Ok zo muje muyi dinner Daddy da Anisah (auta
'yar shekara uku) suna jiranmu."
"Ok." Yace a yayinda ya d'auki jirginsa ya bi
bayan Mummy....
Kan dinning suka nufa inda Daddy da Anisah ke
zaune suna labari harda dariya, zama sukayi itada
Faruk
da Daddy ke musu fira a yayinda Mummy ta zuba
ma kowa abincinsa. Wurin kuma yayi tsit sai
k'arar spoon ake ji. Anisah ce ta katse shirun ta
hanyar jefo ma Daddy tambaya.
"Daddy idan na girma me zan zama?"
Daddy dake shirin kai loma a bakinsa ya dakata
yana kallon Anisah kafin kuma yace
"Anisah kenan, duk abinda kike so shi zaki zama
ay."
Anisah tayi dariya
"Ni banason na zama komai nafiso na shiga
aljanna."
Kowa a wurin sai da ya maida hankalinsa gareta
kafin kuma Mummy tace
"Insha Allah zamu shiga aljanna kinji ko?"
Mummy tace
"Abban Faruk ya batun baka manager d'in ko sun
fasa?"
Daddy yayi murmushi
"Ba fasawa sukayi ba Reemah, sai sun duba
cancanta kafin su bada, idan na dace a bani
manager zasu bani, idan kuma wani ya dace a ba
za'a bashi."
Tayi murmushi
"Haka ne kuma, nidai fatana Allah ya baka sa'a a
dukkan lamuranka"
Yaji dad'in addu'ar matarsa ba kad'an ba, abinda
ke k'ara masa sonta kenan kullum cikin yi masa
addu'a takeyi yana murmushi yace
"Amin ya Allah Reemah."
"Ka fidda ranar da zamu tafi Disney world d'in
kuwa?"
Reemah tace bayan ta had'iye abincin dake
bakinta. Daddy ya sha cup d'in Apple juice kafin
yace
"Eh zuwa upper week dai insha Allah lokacin su
Faruk sun gama exams a islamiyya."
"Yeeyy! Mummy Disney world zamuje da gaske?"
Mummy tayi murmushi tace
"Eh Mamana ko bazaki ba?"
Anisah ta zum6ura baki
"O'o ni zanje."
Faruk yace
"Kalle ta to baza'a dake ba."
Anisha ta sa kuka
"Daddy wai baza'a je dani ba?"
Daddy yayi murmushi
"Ya isa yace bazaki ba, ay kece head d'in tafiyar
gaba d'aya zamu iya barinsa amma ke bazamu
iya barinki ba."
Gwalo ta ma Faruk tana share hawayenta. Faruk
yasa dariya. Anisah tasa kuka.
"Mummy kinga Ya Faruk na min dariya ko?"
Mummy ta harari Faruk
"Zaka fara ko Baba na? Meyasa kakeson ganin
kukan k'anwarka ne?"
Yayi dariya
"Aww dariya ma kakeyi Faruk? Bazaka bata
hak'uri ba?''
Ya buga k'afa.
"Wannan 'yar yarinyar zan ba hak'uri? Tab bazan
bada ba."
Daddy yace
"Just say sorry Faruk, you know she won't stop
crying unless you apologize."
Mummy tace
"Oya Faruk now!"
"Ok sorry!"
Take ta bar kukan inda kuma ta cigaba da cin
abincinta kafin kuma ta kalli Daddy
"Daddy zansha ice cream."
Mummy tace
"Me nace miki akan zak'i?"
Anisah ta turo baki
"O'o ni zansha."
Mummy zata k'ara magana Daddy ya d'aga mata
hannu
"Ba ruwanki Reemah, zan siya mata ice cream."
Anisah tashi tayi da gudu ta wuce parlor tana
tsallen dad'i.
Daddy yayi dariya Mummy na taya shi tace
"Anisah kenan, badai rigima ba."
Daddy yayi dariya
"Lokacinta ne, kema kinyi naki ay."
Mummy tace
"Daddy Faruk fa na wurin."
Yayi dariya
"To sai me? Sai na fad'i abubuwan da kikayi ay"
Da sauri ta tashi tana fad'in
"Haba Daddy!"
Yayi dariya
"Kina tantama ne? Bari kiga..."
Kafin ya k'arasa tayi sama da sauri tana dariya.
Daddy ya tashi ya bi bayanta
"Guduwa kikayi Reemah!"
Faruk tsayawa kallonsu yayi yana dariya cikin
ransa yace
"Allah ka k'ara had'a kanmu what a lovely family!"
***
Meenah na zaune kan carpet tana wasa da abin
wasanta haka kawai kuma sai tasa kuka, Bilki
dake zaune saman kujera tana shan rake tana
kallon wani movie da take so kukan Meenah ya
cika mata kunne. Tsawa ta daka mata
"Ke da Allah kiyi mana shiru yarinya sai shegen
kuka haba!"
Abinka ga yaro wannan tsawa da aka daka mata
ita ta firgita ta yasa ta k'ara fashewa da wani irin
kuka. Haushi ya cika Bilki yasa ta tashi tayi
shigewarta d'aki ta bar Meenah nan na ta faman
kuka kamar zata shid'e. Meenah tayi kuka baiwar
Allah har ta gaji. Nan ta kwanta k'asa tayi ta ajiyar
zuciya har baccin wahala ya kwashe ta a nan.
Bilki na kwance a d'aki ta jiyo k'arar shigowar
motar Alhaji. Da sauri ta fito tazo ta d'auki
Meenah dake a k'asa ta rungume ta tare da zama
kan kujera tana rirriga ta.
Haka Hamza ya shigo ya same ta, da murmushi a
saman fuskarsa ya k'araso. Yana zama Bilki ta
kalle shi
"Sannu da zuwa Alhaji."
Yana murmushi yace
"Yauwa sannu da aiki Bilki, Meenah bacci akeyi?"
Tayi murmushi
"Eh wallahi yanzu ta gama rigima sai na rirrriga ta
tayi bacci."
Yayi murmushi
"Meenah kenan, ay batada rigima ma k'ila dai
baccin takeji daman."
Tayi yak'e
"Sosai ma ay Meenah baiwar Allah ce batada
rigima."
Yace
"Hakane Allah ya raya mana ita."
Tace
"Amin."
Yace
"Bari naje na watsa ruwa na gaji."
Tace
"Ok sai ka fito."
Tana ganin shigewarsa ta kalli Meenah taja dogon
tsaki, sannan taje ta kwantar da ita a d'akin
Meenah d'in kan gado.
Bayan Alhaji ya gama wanka suna zaune kan
dinning suna cin abinci ya kalli Bilki yace
"Bilki a gaskiya ba abinda zance miki sai dai nace
Allah ya saka da alkhairi akan aikin ladar da
kikeyi. Allah ya baki lada."
Ta kalli Alhaji tace
"Haba Alhaji meye na godiya ay yi wa kaine, kuma
ma Meenah kamar d'iyar dana haifa haka na
d'auke ta. Idan har kana min godiya sai naji
kamar baka d'auke ta a matsayin 'yar cikina ba."
Yayi murmushin jin dad'i
"Wallahi ko kusa ba haka bane, kawai dai na yaba
da k'ok'arinki."
Tayi dariya
"Allah sarki. Uhm uhm Alhaji dama madararta da
pampers sun k'are shine nace ya kamata a bad a
siyo mata wasu."
Yace
"Wannan ba damuwa zan baki isashen kud'i ki
siyo mata wanda zai dad'e, naga kamar tafison
madarar ma akan abinci."
Tace
"Hakane."
Bayan sun gama ya d'auko kud'i har dubu goma
ya bata. Amsa tayi tace
"Shikenan zanje na siyo mata.
Yace
"Toh ko ki bari idan na fita na siyo mata mana."
Da sauri tace
"Kai haba kai ina kake da lokaci? Ni da nake gida
kullum ka bari zan siyo mata."
Yayi murmushi
"Toh shikenan."
***
Watan haihuwar Bilki ya kama. Kullum sai ta
tambaye shi kud'in siyayya bai ta6a hana ta ba
saboda har ga Allah ya d'auka Bilki ta shiryu.
Wata rana nak'uda ta kama Bilki gadan gadan,
Hamza ya kaita asibiti, suna zuwa ba'a jima ba ta
haifi 'ya mace. Kyakkyawa fara tas mai k'oshin
lafiya.
Haka aka cigaba da zaman barka inda komai
Hamza yayi mata daidai gwargwado komai yana
tafiya daidai.
Ranar suna yarinya taci sunan kakarta ta wurin
Hamza wato Fatima. Haka aka gama taron suna
aka watse lafiya kowa ya koma gidansa....
Share:

No comments:

Post a Comment