AUREN FANSA CHAPTER 7 & 8
Fatima Zarah fara ce tas sa6anin Meenah da take
ba fara ba tas, murna a wurin Bilki ba'a magana
don yanzu gani take wata sabuwar dama ce ta
samu ta yadda zata dinga samun kud'i a hannun
Alhaji ba tare da wani matsala ba.
Kulawa ta musamman take samu a wurin
mahaifiyarta wadda takeji kamar ta had'iye don
so. A idon Alhaji kuwa had'awa takeyi da Meenah
tana kulawa dasu wanda bata gajiya, bayan
idonsa kuwa Meenah bata samun wata kulawa,
tun daga kan wanka, chanza pampers, cin
abincinta, chanza kaya idan sun 6aci sam bata
damu ba. Sai Alhaji ya kusa dawowa take tashi
tayi mata wanka ta bata abinci yadda komai
tsiyarshi baya ganewa. Zarah kuwa sai ayi mata
wanka sau uku, abinci kuwa duk bayan awa uku
ake bata, sheyasa tun kafin suyi arba'in ta takura
tayi k'iba tayi fam, kamar balloon.
Watan Zarah biyu a duniya Meenah ta shekara
d'aya cas. Tayi kyau tayi wayau abinta. Gata ta
iya magana ba abinda bata fad'i kai kace 'yar
shekara uku. Yadda ta taso ta d'auka Bilki ce
mahaifiyar haka ma Alhaji ne babanta sai dai tafi
shak'uwa da Alhaji saboda muddin yana gida to
suna tare. Sheyasa yanzu idan zai fita sai da
wayau saboda ta dinga kuka kenan kamar zata
sik'e.
***
Ranar wata juma'a Alhaji ya dawo fuskarsa a
cinkushe daga gani yana cikin damuwa, yana
shigowa gaban Bilki ya yanke ya fad'i dama da
safe ya fad'a mata ana neman sa banki don haka
tana ta murna don tasan mijinta ya zama manager
na banki. Yana fita ta hau gyaran gida tayi ma su
Zarah wanka tayi masu kwalliya sosai. Ta shirya
abinci mai rai da lafiya kafin k'arfe d'aya ta gama
komai tana zaman jiransa ya dawo.
Yana shigowa ta tare sa daga bakin k'ofa tana ta
murna kamar zata shige cikin jikinshi. Sai dai kula
da yanayinsa ya sanya jikinta yin sanyi lak'was.
Bayan sun zauna ta fara tambayarsa.
"Alhaji wai ya ake ciki ne? Baka ce komai bafa."
Ya kalle ta na 'yan second kad'an kafin ya
numfasa yace
"Bani akaba ba abokin aikina aka ba."
Dafe k'irji tayi tare da zaro idanu waje. Tace
"Me kace? Kana nufin basu baka ba? Haba !
Gaskiya ba'ayi adalci ba sam."
Yayi murmushi
"Bilkisu kenan, ni banga abin d'aga hankali a nan
ba, kar ki manta komai na duniya rabo ne, idan
bakada rabo komin yadda kakeson abu bazaka
same shi ba."
Shiru tayi tana ayyanawa a ranta. "To wa aka ba?"
Ta tambayi kanta.
"Alhaji Adam Ishaq." Aka ba.
Tashi tayi tsaye
"Haba yanzu kayi magana, ay daman na dad'e da
sanin sun fison su ba Adam, saboda shi yafika
kud'i ko?"
"Haba Bilki! Bana son tashin hankali tunda an riga
an bashi kina da yadda zakiyi ne? Ni ban damu
ba kuma na taya sa murna nima idan lokacin
nawa yazo zan samu. Alhaji Adam mutumin kirki
ne, kuma muna mutunci dashi don haka na taya
sa murna sosai, ke kuma idan na k'ara jin
maganar nan kin tada ita a bakin aurenki!"
Dole taja bakinta tayi shiru, amma tana nan tana
jira ya fita ta kira aminiyarta Hajiya Laila ta fad'a
mata wannan mummunan labarin.
Aiko ana gama sallar magriba ya fice daga gidan,
yana fita ta kira k'awarta Laila tana d'auka Bilki
tac ce
"Wai bakisan meya faru damu ba ko?"
Hajiya Laila cikin d'aga murya tace
"Meyafaru?"
Nan Bilki ta kwashi komai ta fad'a mata tana
gama magana Laila tace
"Ke iya nan kina sani kenan? Tab! Alhaji Adam dai
an amsa transfer zuwa Abuja kiji in fad'a maki,
yayi kud'i abinsa dama kinsan mahashuk'in mai
kud'i ne ba kad'an ba."
Bilki ta zaro idanu waje kamar Laila na ganinta
tace
"Haba ki bari Laila, ta yaya akayi kika sani?"
Laila tayi shewa tace
"Kina nufin baki sani ba? To bari in tak'aice maki
labari Alhaji Adam Ishaq babban d'an kasuwa ne,
sannan yana saida motoci ke kampanin k'era
motoci ke gareshi a k'asashe daban daban.
Bayan nan ga super market da yake dasu ba
iyaka, ga gidajen mai nan tun daga nan Katsina,
Kaduna, Abuja ke babu inda babu. Matarsa ma
shagon saida kayayyaki ke gareta babu abinda
babu k'atuwar mall ce sai dai kin gani."
Bilki da jikinta yayi sannan taji maganar kud'i
yasa tace
"Wai da gaske kike?"
Laila tace
"Ba maganar wasa a nan Hajiya Bilki wallahi
gaskiya na fad'a miki, bakiga kullum basu k'asar
ba? Ke wallahi rayuwarsu abin sha'awa daga shi
sai matarshi sai yaranshi guda biyu kacal ke cin
wannan uban dukiya. Ke suna fantamawa fa.
Kinsan gidanshi dake sabon titin GRA can
wuraren Governor road d'innan ay ko?"
Bilki tace
"Kar dai kice kusa da wannan makarantar premier
boarding school ta mata?"
Laila tace
"Nan fa toh wannan fa, gidanshi nan nan na nisa
sosai, kullum na wuce ta hanyar sai na k'ara
kallon gidan don gidan ya had'u ba kad'an ba."
Bilki tace
"Tabbas na gane gidan, nima ina ganin gidan,
lallai Alhaji Adam ba k'aramin dukiya ya tara
ba..."
Laila tace
"Uhm kedai bari zanzo idan nazo zaki k'arasa jin
sauran bayanan don maganar bata waya bace."
Bilki tace
"Haka ne, gaskiya ina jiranki Laila kar ki shanya
ni."
Laila tayi dariya
"Wallahi zanzo."
"Yaushe to?"
Laila tace
"Zuwa jibi."
Bilki tace
"Ina jiranki."
Daga haka sukayi sallama zuciyar Bilki cike da
tunani kala kala, da kuma sha'awar dukiyar Alhaji
inama ace tata ce, abinda take ta ayyanawa a
ranta kenan.
BAYAN KWANA BIYU
Da safe wuraren k'arfe sha d'aya Laila ta diro
gidan Bilki, aiko murna a wurin Bilki ba'a magana,
nan aka kawo mata kayan motsa baki. Bayan sun
gama gaisawa Laila tace
"Bilkisu mai gadon zinari kenan, yau gani nazo a
gidanki akan labarin da kikeson ji, wato maganar
kud'i."
Bilki tace
"Ina jinki k'awata."
Laila tace
"Ay kamar yadda na fad'a miki rannan toh haka
maganar take, kuma zuwa nan da sati d'aya zasu
tattara su bar garinnan. Niko inada shawara
amma bansani ba ko zaki yarda da ita."
Bilki tace
"Fad'i shawararki."
Laila ta gyara zama bayan ta shanye lemon da ke
cikin glass cup ta soma magana.
"Bilki tunda kinga dani dake duk muna son kud'i
me zai hana mu had'a k'arfi da k'arfi mu k'waci
dukiyar Alhaji Adam."
Bilki ta zaro idanu waje
"Kamar ya? Ban fahimce ki ba."
Laila tayi dariya
"Abinda nake nufi a nan shine, mu had'a k'arfi
nida ke mu k'waci dukiyar Alhaji Adam koda
hakan na nufi mu kashe su."
Da sauri Bilki ta zabura had'e da zaro idanu waje
tana kallon Hajiya Laila...
Laila ce ta cigaba da magana.
"Ko dai har yanzu baki fahimta ba ne?"
Ajiyar zuciya Bilki tayi, sannan tace
"A gaskiya Laila ban iyawa, kisa fa kika ce? Don
ina son dukiya sai akace na kashe su, gaskiya mu
chanza shawara dai."
Laila tayi kwafa.
"To sai akace mu zamu bisu mu aikata
k'udirinmu? Ko kusa ba haka nake nufi ba, abinda
nake nufi a nan shine..."
Nan naga ta rad'a mata wata magana daga
k'arshe dukkansu suka kwashe da dariya.
Bilki tana dariya tace
"Shegiyar gari, lallai Laila sai dai a barki amma ke
shu'uma ce wallahi."
Hajiya Laila ta k'yalk'yale da dariya sosai sannan
tace
"Kema haka."
Bilki ta tashi tana gyara zaman d'ankwalinta tana
kallon Laila tace
"Kamar naji kuman Zarah bari na dubo ta."
Laila tace
"Yi sauri kuwa nima naji."
Jim kad'an sai ga Bilki ta shigo da Zarah a
hannunta da alama yanzu Zaran ta tashi daga
bacci, tana zuwa Laila ta mik'a hannu ta fara mata
wasa, can sai ga Meenah ta fito da alama bacci ta
tashi don kuwa kanta buzu buzu yake, saboda
yanayin gashinta mai cika kuma ga tsawo sheyasa
ko ya ta kwanta sai yayi buzu buzu. Zuwa tayi
kusa da Bilki tana murza idanu. Su kuwa sai
faman ta6e baki sukeyi. Meenah tace
"Maama wunwa."
Laila ta ta6e baki tace
"Uban me tace?"
Bilki tace
"Ohon mata, ke tafi can ki bamu wuri."
Abinka ga yaro da ba ganewa tayi ba, sai ma ta
matso kusa da Bilki ta jingina da ita. Da sauri
Bilkin ta hankad'e ta gefe ta fad'i k'asa tim!
"Wannan yarinya anyi mayya! Mts." Cewar Laila
had'e da jan tsaki.
Bilki ta jawo hannunta da k'arfi, Meenah ta fashe
da kuka.
Kitchen suka nufa ta had'a mata tea a cup tana
tsaki sannan ta dire mata k'asa.
"Oya zauna kisha yarinya bata aje komai ba sai
ci? Haba!" Nan ta zauna ta shanye tas sannan ta
fito daga kitchen d'in.
Tana gama fad'an haka ta fice taje ta had'o ma
Zarah cereal ta koma parlor, Laila ke bata har ta
kammala sannan aka bata ruwa.
A tare suka girka abincin rana inda Laila tayi ma
Zarah wanka, sannan suka dafa fried rice da
papered chicken sai had'ad'en salad. Wuraren
uku da kwata Laila tayi sallama da Bilki ta tafi
gida.
Sai wurin biyar saura sannan Bilki tayi ma Meenah
wanka ta bata abincin rana.
Kamar kullum bayan Alhaji ya dawo gida yayi
wanka yaci abinci, suka zauna palor suna 'yar fira
kafin a kira sallar magrib. Kasancewar Meenah
batasan dawowar Baban nata ba, tana can d'aki
tana wasa. Sai data fito, aiko tana ganin shi ta
rugo da d'an gudunta ta zo kusa da shi tana
fad'in
"Dada!"
Cike da jin dad'i Alhaji yace
"D'iyar Dada ashe ana ciki, zo nan."
Tana zuwa ya d'auke ta ya zaunar kan cinyarsa
yana mata surutu tana dariya. Can kuma sai tace
"Dada kaga Maama ta bije ni d'azu."
Ya ware idanu
"Me kikayi wa Maama ta bige ki?"
Tayi shiru tana kallonsa can tace
"Bakomai."
Bilki ta taso tana dariya tace
"Kai yaro ma dai daban ne, d'azu ne fa na shiga
wanka nazo na iske ta tana zubar da madara,
shine fa nace mata kar ta k'ara. Alhaji yayi dariya
"Ah ah Meenah a daina 6arna ba kyau kinji ko?
Idan Maama tace a daina a daina kinji?"
Ta gyad'a kai. Sai kuma yace
"Bilki ya naga Meenah ta rame ne ko bata son cin
abinci?"
Tayi dariya tace
"Ay Alhaji inda kasan yadda nake da fama da
yarinyar nan akan taci abinci ko? Sai kayi mamaki
sam batason ci na rasa dalili."
Yace
"To kuma ya baki sanar dani ba? Muka sani ko
wani abin ke damunta? Kinsan yaro tunda ba
fad'a zatayi ba."
Tace
"To k'ila dai."
Ya juyo da dubansa ga Meenah
"Haba Meenan Dada, meyasa baki cin abinci?"
Nan ma shiru. Yayi murmushi
"Zaki sha ice cream?"
Nan take da washe baki tana murna. Shima yaji
dad'i yace
"Yauwa to bari idan na fita yanzu kafin na dawo
gida zan siyo maki harda biscuit ma."
Saukar da ita yayi daga cinyarsa yace
"Bilki bari na wuce masallaci lokacin sallah yayi
sai na dawo."
Tace
"A dawo lafiya."
Sai da ya fita ta bishi da harara dashi da Meenah
dake tsaye a tsorace gaban Bilki.
Tana huci tace
"Gaskiya abinnan ya fara isa ta, sai wani nan nan
yake da yarinyar nan amma naga ba ruwanshi ma
da Zarah, lallai Alhaji ka haifi d'iya a cikinka
amma ka nuna son d'iyar wata? To da sake mts."
Daga nan ta shige d'aki, Meenah na tsaye tana
zare idanu.
Haka kuwa akayi Alhaji da zai dawo sai da ya
tsaya ya siya ma Meenah ice cream da biscuit sai
ya k'aro mata kayan lashe lashe na yara. Zarah
kuwa wani d'an abin wasa ne na yara ya siya
mata tunda yasan bata isa shan wad'annan kayan
ba.
Yana dawowa Meenah ta tare shi tana murna, ya
bata ice cream d'inta nan ta zauna ta shanye tas
sannan ya bata biscuit d'inta ta tafi d'aki.
Abin wasan yara ya bama Zarah dake hannunsa
yana mata wasa. Ita kuwa sai dariya takeyi. Bilki
na zaune kusa dasu tana wasa da Zarah. Can
Alhaji yace
"Ina Meenah tayi ne?"
Tayi tsaki a ranta tace
"Yanzu ta tafi d'aki ay ta ga k'wad'ayi kuma tunda
bazata ci abinci ba."
Tashi yayi yana fad'in
"Ina zuwa."
Ta6e baki tayi tana mai jin haushin Meenah.
Yana shiga d'aki ya ishe Meenah kwance k'asa da
biscuit a hannunta bacci ya kwashe ta. Murmushi
yayi ya d'auko ta ya d'ora ta kan gado, ya gyara
mata kwanciya sannan ya kashe fitilar ya fito.
Koda ya fito Bilki bata nuna komai ba, Zarah ta
k'ar6a tayi d'aki da ita don yi mata wanka.
BAYAN KWANA BIYU
Bilki ta fito wanka da safe kiran Laila ya shigo,
tana d'auka Laila tafara magana
"Kash Hajiya Bilki yanzu naji labarin iyalen Alhaji
Adam sun koma Abuja gaba d'aya."
Da sauri Bilki tace
"Haba dai? To yanzu ya kenan?"
"Bansani ba nima, plan d'inmu ya rushe don
gidansa na Abuja akwai tsaro sosai, ko ina sojoji
ne a gidan."
Bilki tace
"Gaskiya akwai had'ari mu ce zamuyi wani motsi
yanzu. Amma ki bari tukunna a sake shawara."
"To shikenan." Laila tace tare da katse kiran. Nan
tayi ta sak'a da warwara ta rasa mafita.
***
Haka rayuwar ta cigaba da gudana har akayi
shekara d'aya amma har yau sun rasa wata
mafita.
A lokacin kuma Meenah ta shekara biyu harda
rabi Alhaji ya fara shirye shiryen saka ta
makaranta da kuma islamiyya. Don ya fuskanci
zata iya da wuri don a yadda ya fahimce ta, ta iya
saurin d'aukar abu da kuma maganarta ta fito ga
surutu ba abinda bata fad'i.
Sheyasa ma yanzu Bilki ta rage takura mata don
muddin Alhaji ya dawo zata kwashe komai ta
fad'a masa. Tana gudun kar tun baya tunanin
komai har ya fara zarginta...
Fatima Zarah fara ce tas sa6anin Meenah da take
ba fara ba tas, murna a wurin Bilki ba'a magana
don yanzu gani take wata sabuwar dama ce ta
samu ta yadda zata dinga samun kud'i a hannun
Alhaji ba tare da wani matsala ba.
Kulawa ta musamman take samu a wurin
mahaifiyarta wadda takeji kamar ta had'iye don
so. A idon Alhaji kuwa had'awa takeyi da Meenah
tana kulawa dasu wanda bata gajiya, bayan
idonsa kuwa Meenah bata samun wata kulawa,
tun daga kan wanka, chanza pampers, cin
abincinta, chanza kaya idan sun 6aci sam bata
damu ba. Sai Alhaji ya kusa dawowa take tashi
tayi mata wanka ta bata abinci yadda komai
tsiyarshi baya ganewa. Zarah kuwa sai ayi mata
wanka sau uku, abinci kuwa duk bayan awa uku
ake bata, sheyasa tun kafin suyi arba'in ta takura
tayi k'iba tayi fam, kamar balloon.
Watan Zarah biyu a duniya Meenah ta shekara
d'aya cas. Tayi kyau tayi wayau abinta. Gata ta
iya magana ba abinda bata fad'i kai kace 'yar
shekara uku. Yadda ta taso ta d'auka Bilki ce
mahaifiyar haka ma Alhaji ne babanta sai dai tafi
shak'uwa da Alhaji saboda muddin yana gida to
suna tare. Sheyasa yanzu idan zai fita sai da
wayau saboda ta dinga kuka kenan kamar zata
sik'e.
***
Ranar wata juma'a Alhaji ya dawo fuskarsa a
cinkushe daga gani yana cikin damuwa, yana
shigowa gaban Bilki ya yanke ya fad'i dama da
safe ya fad'a mata ana neman sa banki don haka
tana ta murna don tasan mijinta ya zama manager
na banki. Yana fita ta hau gyaran gida tayi ma su
Zarah wanka tayi masu kwalliya sosai. Ta shirya
abinci mai rai da lafiya kafin k'arfe d'aya ta gama
komai tana zaman jiransa ya dawo.
Yana shigowa ta tare sa daga bakin k'ofa tana ta
murna kamar zata shige cikin jikinshi. Sai dai kula
da yanayinsa ya sanya jikinta yin sanyi lak'was.
Bayan sun zauna ta fara tambayarsa.
"Alhaji wai ya ake ciki ne? Baka ce komai bafa."
Ya kalle ta na 'yan second kad'an kafin ya
numfasa yace
"Bani akaba ba abokin aikina aka ba."
Dafe k'irji tayi tare da zaro idanu waje. Tace
"Me kace? Kana nufin basu baka ba? Haba !
Gaskiya ba'ayi adalci ba sam."
Yayi murmushi
"Bilkisu kenan, ni banga abin d'aga hankali a nan
ba, kar ki manta komai na duniya rabo ne, idan
bakada rabo komin yadda kakeson abu bazaka
same shi ba."
Shiru tayi tana ayyanawa a ranta. "To wa aka ba?"
Ta tambayi kanta.
"Alhaji Adam Ishaq." Aka ba.
Tashi tayi tsaye
"Haba yanzu kayi magana, ay daman na dad'e da
sanin sun fison su ba Adam, saboda shi yafika
kud'i ko?"
"Haba Bilki! Bana son tashin hankali tunda an riga
an bashi kina da yadda zakiyi ne? Ni ban damu
ba kuma na taya sa murna nima idan lokacin
nawa yazo zan samu. Alhaji Adam mutumin kirki
ne, kuma muna mutunci dashi don haka na taya
sa murna sosai, ke kuma idan na k'ara jin
maganar nan kin tada ita a bakin aurenki!"
Dole taja bakinta tayi shiru, amma tana nan tana
jira ya fita ta kira aminiyarta Hajiya Laila ta fad'a
mata wannan mummunan labarin.
Aiko ana gama sallar magriba ya fice daga gidan,
yana fita ta kira k'awarta Laila tana d'auka Bilki
tac ce
"Wai bakisan meya faru damu ba ko?"
Hajiya Laila cikin d'aga murya tace
"Meyafaru?"
Nan Bilki ta kwashi komai ta fad'a mata tana
gama magana Laila tace
"Ke iya nan kina sani kenan? Tab! Alhaji Adam dai
an amsa transfer zuwa Abuja kiji in fad'a maki,
yayi kud'i abinsa dama kinsan mahashuk'in mai
kud'i ne ba kad'an ba."
Bilki ta zaro idanu waje kamar Laila na ganinta
tace
"Haba ki bari Laila, ta yaya akayi kika sani?"
Laila tayi shewa tace
"Kina nufin baki sani ba? To bari in tak'aice maki
labari Alhaji Adam Ishaq babban d'an kasuwa ne,
sannan yana saida motoci ke kampanin k'era
motoci ke gareshi a k'asashe daban daban.
Bayan nan ga super market da yake dasu ba
iyaka, ga gidajen mai nan tun daga nan Katsina,
Kaduna, Abuja ke babu inda babu. Matarsa ma
shagon saida kayayyaki ke gareta babu abinda
babu k'atuwar mall ce sai dai kin gani."
Bilki da jikinta yayi sannan taji maganar kud'i
yasa tace
"Wai da gaske kike?"
Laila tace
"Ba maganar wasa a nan Hajiya Bilki wallahi
gaskiya na fad'a miki, bakiga kullum basu k'asar
ba? Ke wallahi rayuwarsu abin sha'awa daga shi
sai matarshi sai yaranshi guda biyu kacal ke cin
wannan uban dukiya. Ke suna fantamawa fa.
Kinsan gidanshi dake sabon titin GRA can
wuraren Governor road d'innan ay ko?"
Bilki tace
"Kar dai kice kusa da wannan makarantar premier
boarding school ta mata?"
Laila tace
"Nan fa toh wannan fa, gidanshi nan nan na nisa
sosai, kullum na wuce ta hanyar sai na k'ara
kallon gidan don gidan ya had'u ba kad'an ba."
Bilki tace
"Tabbas na gane gidan, nima ina ganin gidan,
lallai Alhaji Adam ba k'aramin dukiya ya tara
ba..."
Laila tace
"Uhm kedai bari zanzo idan nazo zaki k'arasa jin
sauran bayanan don maganar bata waya bace."
Bilki tace
"Haka ne, gaskiya ina jiranki Laila kar ki shanya
ni."
Laila tayi dariya
"Wallahi zanzo."
"Yaushe to?"
Laila tace
"Zuwa jibi."
Bilki tace
"Ina jiranki."
Daga haka sukayi sallama zuciyar Bilki cike da
tunani kala kala, da kuma sha'awar dukiyar Alhaji
inama ace tata ce, abinda take ta ayyanawa a
ranta kenan.
BAYAN KWANA BIYU
Da safe wuraren k'arfe sha d'aya Laila ta diro
gidan Bilki, aiko murna a wurin Bilki ba'a magana,
nan aka kawo mata kayan motsa baki. Bayan sun
gama gaisawa Laila tace
"Bilkisu mai gadon zinari kenan, yau gani nazo a
gidanki akan labarin da kikeson ji, wato maganar
kud'i."
Bilki tace
"Ina jinki k'awata."
Laila tace
"Ay kamar yadda na fad'a miki rannan toh haka
maganar take, kuma zuwa nan da sati d'aya zasu
tattara su bar garinnan. Niko inada shawara
amma bansani ba ko zaki yarda da ita."
Bilki tace
"Fad'i shawararki."
Laila ta gyara zama bayan ta shanye lemon da ke
cikin glass cup ta soma magana.
"Bilki tunda kinga dani dake duk muna son kud'i
me zai hana mu had'a k'arfi da k'arfi mu k'waci
dukiyar Alhaji Adam."
Bilki ta zaro idanu waje
"Kamar ya? Ban fahimce ki ba."
Laila tayi dariya
"Abinda nake nufi a nan shine, mu had'a k'arfi
nida ke mu k'waci dukiyar Alhaji Adam koda
hakan na nufi mu kashe su."
Da sauri Bilki ta zabura had'e da zaro idanu waje
tana kallon Hajiya Laila...
Laila ce ta cigaba da magana.
"Ko dai har yanzu baki fahimta ba ne?"
Ajiyar zuciya Bilki tayi, sannan tace
"A gaskiya Laila ban iyawa, kisa fa kika ce? Don
ina son dukiya sai akace na kashe su, gaskiya mu
chanza shawara dai."
Laila tayi kwafa.
"To sai akace mu zamu bisu mu aikata
k'udirinmu? Ko kusa ba haka nake nufi ba, abinda
nake nufi a nan shine..."
Nan naga ta rad'a mata wata magana daga
k'arshe dukkansu suka kwashe da dariya.
Bilki tana dariya tace
"Shegiyar gari, lallai Laila sai dai a barki amma ke
shu'uma ce wallahi."
Hajiya Laila ta k'yalk'yale da dariya sosai sannan
tace
"Kema haka."
Bilki ta tashi tana gyara zaman d'ankwalinta tana
kallon Laila tace
"Kamar naji kuman Zarah bari na dubo ta."
Laila tace
"Yi sauri kuwa nima naji."
Jim kad'an sai ga Bilki ta shigo da Zarah a
hannunta da alama yanzu Zaran ta tashi daga
bacci, tana zuwa Laila ta mik'a hannu ta fara mata
wasa, can sai ga Meenah ta fito da alama bacci ta
tashi don kuwa kanta buzu buzu yake, saboda
yanayin gashinta mai cika kuma ga tsawo sheyasa
ko ya ta kwanta sai yayi buzu buzu. Zuwa tayi
kusa da Bilki tana murza idanu. Su kuwa sai
faman ta6e baki sukeyi. Meenah tace
"Maama wunwa."
Laila ta ta6e baki tace
"Uban me tace?"
Bilki tace
"Ohon mata, ke tafi can ki bamu wuri."
Abinka ga yaro da ba ganewa tayi ba, sai ma ta
matso kusa da Bilki ta jingina da ita. Da sauri
Bilkin ta hankad'e ta gefe ta fad'i k'asa tim!
"Wannan yarinya anyi mayya! Mts." Cewar Laila
had'e da jan tsaki.
Bilki ta jawo hannunta da k'arfi, Meenah ta fashe
da kuka.
Kitchen suka nufa ta had'a mata tea a cup tana
tsaki sannan ta dire mata k'asa.
"Oya zauna kisha yarinya bata aje komai ba sai
ci? Haba!" Nan ta zauna ta shanye tas sannan ta
fito daga kitchen d'in.
Tana gama fad'an haka ta fice taje ta had'o ma
Zarah cereal ta koma parlor, Laila ke bata har ta
kammala sannan aka bata ruwa.
A tare suka girka abincin rana inda Laila tayi ma
Zarah wanka, sannan suka dafa fried rice da
papered chicken sai had'ad'en salad. Wuraren
uku da kwata Laila tayi sallama da Bilki ta tafi
gida.
Sai wurin biyar saura sannan Bilki tayi ma Meenah
wanka ta bata abincin rana.
Kamar kullum bayan Alhaji ya dawo gida yayi
wanka yaci abinci, suka zauna palor suna 'yar fira
kafin a kira sallar magrib. Kasancewar Meenah
batasan dawowar Baban nata ba, tana can d'aki
tana wasa. Sai data fito, aiko tana ganin shi ta
rugo da d'an gudunta ta zo kusa da shi tana
fad'in
"Dada!"
Cike da jin dad'i Alhaji yace
"D'iyar Dada ashe ana ciki, zo nan."
Tana zuwa ya d'auke ta ya zaunar kan cinyarsa
yana mata surutu tana dariya. Can kuma sai tace
"Dada kaga Maama ta bije ni d'azu."
Ya ware idanu
"Me kikayi wa Maama ta bige ki?"
Tayi shiru tana kallonsa can tace
"Bakomai."
Bilki ta taso tana dariya tace
"Kai yaro ma dai daban ne, d'azu ne fa na shiga
wanka nazo na iske ta tana zubar da madara,
shine fa nace mata kar ta k'ara. Alhaji yayi dariya
"Ah ah Meenah a daina 6arna ba kyau kinji ko?
Idan Maama tace a daina a daina kinji?"
Ta gyad'a kai. Sai kuma yace
"Bilki ya naga Meenah ta rame ne ko bata son cin
abinci?"
Tayi dariya tace
"Ay Alhaji inda kasan yadda nake da fama da
yarinyar nan akan taci abinci ko? Sai kayi mamaki
sam batason ci na rasa dalili."
Yace
"To kuma ya baki sanar dani ba? Muka sani ko
wani abin ke damunta? Kinsan yaro tunda ba
fad'a zatayi ba."
Tace
"To k'ila dai."
Ya juyo da dubansa ga Meenah
"Haba Meenan Dada, meyasa baki cin abinci?"
Nan ma shiru. Yayi murmushi
"Zaki sha ice cream?"
Nan take da washe baki tana murna. Shima yaji
dad'i yace
"Yauwa to bari idan na fita yanzu kafin na dawo
gida zan siyo maki harda biscuit ma."
Saukar da ita yayi daga cinyarsa yace
"Bilki bari na wuce masallaci lokacin sallah yayi
sai na dawo."
Tace
"A dawo lafiya."
Sai da ya fita ta bishi da harara dashi da Meenah
dake tsaye a tsorace gaban Bilki.
Tana huci tace
"Gaskiya abinnan ya fara isa ta, sai wani nan nan
yake da yarinyar nan amma naga ba ruwanshi ma
da Zarah, lallai Alhaji ka haifi d'iya a cikinka
amma ka nuna son d'iyar wata? To da sake mts."
Daga nan ta shige d'aki, Meenah na tsaye tana
zare idanu.
Haka kuwa akayi Alhaji da zai dawo sai da ya
tsaya ya siya ma Meenah ice cream da biscuit sai
ya k'aro mata kayan lashe lashe na yara. Zarah
kuwa wani d'an abin wasa ne na yara ya siya
mata tunda yasan bata isa shan wad'annan kayan
ba.
Yana dawowa Meenah ta tare shi tana murna, ya
bata ice cream d'inta nan ta zauna ta shanye tas
sannan ya bata biscuit d'inta ta tafi d'aki.
Abin wasan yara ya bama Zarah dake hannunsa
yana mata wasa. Ita kuwa sai dariya takeyi. Bilki
na zaune kusa dasu tana wasa da Zarah. Can
Alhaji yace
"Ina Meenah tayi ne?"
Tayi tsaki a ranta tace
"Yanzu ta tafi d'aki ay ta ga k'wad'ayi kuma tunda
bazata ci abinci ba."
Tashi yayi yana fad'in
"Ina zuwa."
Ta6e baki tayi tana mai jin haushin Meenah.
Yana shiga d'aki ya ishe Meenah kwance k'asa da
biscuit a hannunta bacci ya kwashe ta. Murmushi
yayi ya d'auko ta ya d'ora ta kan gado, ya gyara
mata kwanciya sannan ya kashe fitilar ya fito.
Koda ya fito Bilki bata nuna komai ba, Zarah ta
k'ar6a tayi d'aki da ita don yi mata wanka.
BAYAN KWANA BIYU
Bilki ta fito wanka da safe kiran Laila ya shigo,
tana d'auka Laila tafara magana
"Kash Hajiya Bilki yanzu naji labarin iyalen Alhaji
Adam sun koma Abuja gaba d'aya."
Da sauri Bilki tace
"Haba dai? To yanzu ya kenan?"
"Bansani ba nima, plan d'inmu ya rushe don
gidansa na Abuja akwai tsaro sosai, ko ina sojoji
ne a gidan."
Bilki tace
"Gaskiya akwai had'ari mu ce zamuyi wani motsi
yanzu. Amma ki bari tukunna a sake shawara."
"To shikenan." Laila tace tare da katse kiran. Nan
tayi ta sak'a da warwara ta rasa mafita.
***
Haka rayuwar ta cigaba da gudana har akayi
shekara d'aya amma har yau sun rasa wata
mafita.
A lokacin kuma Meenah ta shekara biyu harda
rabi Alhaji ya fara shirye shiryen saka ta
makaranta da kuma islamiyya. Don ya fuskanci
zata iya da wuri don a yadda ya fahimce ta, ta iya
saurin d'aukar abu da kuma maganarta ta fito ga
surutu ba abinda bata fad'i.
Sheyasa ma yanzu Bilki ta rage takura mata don
muddin Alhaji ya dawo zata kwashe komai ta
fad'a masa. Tana gudun kar tun baya tunanin
komai har ya fara zarginta...


No comments:
Post a Comment